Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
F??ima bint Mu?ammad
(
Larabci
:
???????? ?????? ????????
, 605/15?632 CE), wanda aka fi sani da
F??ima al-Zahr??
(
???????? ???????????
), ta kasance diyar
annabin musulunci
Muhammad
da matarsa
Khadija
.
Mijin Fatima shi ne
Ali
, shine na hudu a cikin
Khalifofin Rashidun
kuma
Imamin Shi'a
na farko . 'Ya'yan Fatima su ne
Hasan
da
Husaini
Imaman Shi'a na biyu da na uku.
An kwatanta Fatima da
Maryamu
mahaifiyar
Isah
, musamman a aqidar Shi'a.
An ce Muhammadu ya dauke ta a matsayin mafificiya a mata
kuma mafi soyuwa a gare shi.
Sau da yawa ana kallonta a matsayin babban abin tarihi ga matan
musulmi
da kuma ita me tausayi, karimci, da jurewa wahala.
Ta hanyar Fatima ne zuriyar Muhammadu suka wanzu har yau.
Sunanta da lakabinta sun kasance sanannen za?i ga 'yan mata musulmai.
Lokacin da Muhammadu ya rasu a shekara ta 632, Fatima da mijinta Ali sun ?i amincewa da mulkin k
halifa
na farko,
Abubakar
. Ma'auratan da magoya bayansu sun yi imanin cewa Ali shi ne mafi cancantar magajin Muhammadu,
mai yiwuwa suna nufin sanarwarsa a Ghadir Khumm .
Rigima ta kunno kai dangane da mutuwar Fatima a cikin watanni shida da mutuwar Muhammadu.
Ahlus Sunna
sun yarda cewa Fatima ta rasu ne da bakin ciki.
A cikin
Shi’a
kuwa, an ce mutuwar Fatima (barin da tayi) ta yi ne kai tsaye sakamakon raunukan da ta samu a lokacin wani farmaki da aka kai gidanta don murkushe Ali, wanda Abubakar ya umarta.
An yi imanin cewa fatawar Fatima da ta rasu shi ne kar khalifa ya halarci jana’izarta.
An binne ta a asirce da daddare kuma ba a tabbatar da ainihin inda aka binne ta ba.
Mafi sanannan la?abinta shi ne al-Zahra ( lit. 'me haskakawa', 'me haske?' ),
wanda ke nuni akan taqawarta da tsayuwarta a cikin addu'a.
Shi'a sun yi imani da wannan taswirar cewa tana nuni ne ga halittarta ta farko daga hasken da ke ci gaba da haskakawa a cikin halittu.
Shi'a Ibn Babawahy ( d.?991 ) ya rubuta cewa, duk lokacin da Fatima ta yi addu'a, haskenta yana haskakawa ga mazauna sama kamar yadda hasken taurari ke haskaka mazaunan duniya.
Sauran lakabin ta a cikin Shi'a su ne al-Shiddiqa ( lit. 'me gaskiyta?' ),
al-Tahira ( lit.?'me tsarki' ),
al-Mubaraka ( lit.?'me albarka' ),
da al-Mansura ( lit.?'wanda Allah ya taimaka' ).
Wani lakabin Shi'a kuma shi ne al-Mu?additha, bisa la'akari da rahoton cewa mala'iku sun yi magana da Fatima a lokuta da dama,
kamar
Maryamu
mahaifiyar
Isah
.